[ad_1]
Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya sallami masu taimaka masa da kuma masu bashi shawara su 252.
Abubakar Shekara , daraktan yada labaran gwamnan shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.
“Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya bayar da umarnin sallamar dukkanin masu taimaka masa daga bakin aiki a gwamnatin jihar da yawansu ya kai 252,” a cewar sanarwar.
Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya yi haka ne domin basu dama su cigaba da shiga al’amuran siyasa.
Gwamnan ya kuma gode su kan aikin da suka yi wa jihar kana ya yi musu fatan alheri akan abinda za su sanya a gaba.
Amma kuma daya daga cikin mutanen da aka sallama mai suna Ibrahim Haske a a wani taron manema labarai yace sun ajiye mukaman nasu ne a kashin kansu .
Haske ya bayyana cewa sun cimma wannan mataki ne biyo bayan sauya shekar da gwamna Tambuwal ya yi daga jam’iyar APC ya zuwa PDP.
[ad_2]