Tambuwal ya sallami masu bashi shawara 252

[ad_1]








Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya sallami masu taimaka masa da kuma masu bashi shawara su 252.

Abubakar Shekara , daraktan yada labaran gwamnan shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

“Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya bayar da umarnin sallamar dukkanin masu taimaka masa daga bakin aiki a gwamnatin jihar da yawansu ya kai 252,” a cewar sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya yi haka ne domin basu dama su cigaba da shiga al’amuran siyasa.

Gwamnan ya kuma gode su kan aikin da suka yi wa jihar kana ya yi musu fatan alheri akan abinda za su sanya a gaba.

Amma kuma daya daga cikin mutanen da aka sallama mai suna Ibrahim Haske a a wani taron manema labarai yace sun ajiye mukaman nasu ne a kashin kansu .

Haske ya bayyana cewa sun cimma wannan mataki ne biyo bayan sauya shekar da gwamna Tambuwal ya yi daga jam’iyar APC ya zuwa PDP.




[ad_2]

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...