Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP).
Tambuwal, wanda ke wakiltar mazabar Sokoto ta Kudu a majalisar dattawa, ya bayyana hakan ne a cikin wata wasiƙa mai kwanan watan 11 ga watan Maris da ya aika wa shugaban jam’iyyar PDP na mazabarsa ta Tambuwal/Shinfiri.
A cikin wasiƙar, ya ce ya yanke shawarar barin jam’iyyar ne sakamakon rikice-rikicen cikin gida da kuma rashin jituwa da ke addabar PDP a matakai daban-daban.
Ya kuma sanar da cewa ya koma sabuwar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).
Tambuwal Ya Fice Daga PDP, Ya Koma ADC

