Tambuwal Ya Fice Daga PDP, Ya Koma ADC

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP).

Tambuwal, wanda ke wakiltar mazabar Sokoto ta Kudu a majalisar dattawa, ya bayyana hakan ne a cikin wata wasiƙa mai kwanan watan 11 ga watan Maris da ya aika wa shugaban jam’iyyar PDP na mazabarsa ta Tambuwal/Shinfiri.

A cikin wasiƙar, ya ce ya yanke shawarar barin jam’iyyar ne sakamakon rikice-rikicen cikin gida da kuma rashin jituwa da ke addabar PDP a matakai daban-daban.

Ya kuma sanar da cewa ya koma sabuwar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

More from this stream

Recomended