Takai ya bijirewa umarnin Kwankwaso

Mai neman takarar kujerar gwamnan jihar Kano karkashin jam’iyar PDP, MAllam Salihu Sagir Takai, ya ki bin umarnin jagoranc jam’iyar na Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya neme shi da ya tsaya takarar kujerar sanatan Kano ta kudu a maimakon takarar gwamna da yake son yi.

Takai ya zabi yin mubaya’a ga bangaren jam’iyar PDP dake biyayya ga Kwankwaso inda yaki yarda ya bi da dadadden jagoransa a siyasance Mallam Ibrahim Shekarau wanda ya koma jam’iyar APC.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa Kwankwaso ya nemi yan takarar gwamnan dake kan gaba a bangarensa wato tsohon mataimakin gwamna, Farfesa Hafiz Abubakar da kuma Mallam Salihu Sagir Takai da su tsaya takarar sanata furucin da bai wa mutane biyun dadi ba.

Ya yin da magoya bayan Hafizu Abubakar suke baya-baya wajen bayyana kin amincewarsu su kuwa magoya bayan Takaivsun fito fili sun nuna adawarsu da tsarin.

Daraktan yakin neman zaben Takai,wato Takai Campaign Organisation, Faruk Iya ya yi kira ga magoya bayansu da su fito su raka shi garin Kaduna domin halartar wurin tantance yan takara.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...