Sojojin Sun Gano Wurin Ƙera Bindiga A Jihar Filato

Sojojin rundunar samar da tsaro a jihar Filato ta Operation Safe Haven sun bankaɗo wata haramtacciyar masana’antar ƙera makamai dake ƙauyen Pakachi a ƙaramar hukumar Mangu ta jihar Filato.

Jami’in ƴada labarai na rundunar, James Oya ya ce sojojin sun gano makamai da dama da kuma harsasai tare da kama mutum guda a farmakin da suka kai masana’antar.

Oya ya ce an samu nasarar gano masana’antar ne sakamakon cigaba da jajircewa da rundunar take na raba jihar da duk wasu ɓata gari dake tayar da zaune tsaye.

Ya ce an gano wurin ne a wani saman tsauni dake kauyen na Pakachi.

Ya ƙara da cewa wanda ake zargin shi ne mai masana’antar ya cika wandonsa da iska amma na cigaba kokarin ganin an kamo shi domin ya fuskanci hukunci.

Bindigogin da aka gano a wurin sun haɗa da AK-47 guda biyar da kuma ƙaramar bindiga ƙirar Pistol guda 11.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...