Sojojin Najeriya sun kashe ƴanta’adda a Arewa maso Yamma

Dakarun sojojin Najeriya a wani samame daban-daban da suka kai a jihohin Zamfara da Katsina sun kashe ‘yan ta’adda 11.

A garin Zamafara, an kai samame maboyar wani shugaban ‘yan ta’adda, Hassan Yantagwaye, a karamar hukumar Tsafe, wanda ya yi sanadin fafatawa da ‘yan ta’addan guda biyu a harin.

Hakan na kunshe ne a wani sako da rundunar sojin Najeriya ta fitar a ranar Litinin.

A cewar saƙon, “Dakarun Sojojin Najeriya da aka tura domin Yaki da Ta’addanci a Jihohin Katsina da Zamfara, a wani jerin hare-hare na hadin gwiwa sun kai farmaki a yankunan ‘yan ta’adda wanda ya yi sanadin kawar da dimbin ‘yan ta’adda.

“A wani samame da suka kai jihar Zamfara, a ranar 29 ga Maris, 2024, sojoji sun yi nasarar kai samame a kogon wani fitaccen sarkin ‘yan ta’adda, Hassan Yantagwaye, a karamar hukumar Tsafe.

“A yayin farmakin, sojoji sun fatattaki ‘yan ta’addan a wani artabu da suka yi da su, inda suka kashe uku daga cikinsu tare da kwato tarin makamai da alburusai.  Sojojin sun kuma lalata sansanonin ‘yan ta’addan.”

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...