Sojojin Najeriya sun hallaka yan ta’addar Boko Haram a Damasak

Rundunar sojan Najeriya ta samu nasara a fafatawar da tayi da yan kungiyar Boko Haram a garin Damasak dake jihar Borno.

Yan kungiyar ta Boko Haram sun kai wani farmaki kan sansanin sojan bataliya ta 145 dake Damasak a karamar hukumar Mobar ta jihar Borno.

A wata sanarwa da rundunar sojan ta fitar ta ce yayan kungiyar ta Boko Haram 7 ne aka kashe ya yin musayar wutar.

Haka kuma sojojin sun samu nasarar lalata motar yan ta’addar da kuma samun makamai da dama.

A yan kwanakin yan kungiyar sun zafafa hare-haren da suke kai wa jami’an tsaro a yankin arewa maso gabashin Najeriya dake fama da rikicin Boko Haram.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...