Rundunar sojan Najeriya ta samu nasara a fafatawar da tayi da yan kungiyar Boko Haram a garin Damasak dake jihar Borno.
Yan kungiyar ta Boko Haram sun kai wani farmaki kan sansanin sojan bataliya ta 145 dake Damasak a karamar hukumar Mobar ta jihar Borno.
A wata sanarwa da rundunar sojan ta fitar ta ce yayan kungiyar ta Boko Haram 7 ne aka kashe ya yin musayar wutar.
Haka kuma sojojin sun samu nasarar lalata motar yan ta’addar da kuma samun makamai da dama.
A yan kwanakin yan kungiyar sun zafafa hare-haren da suke kai wa jami’an tsaro a yankin arewa maso gabashin Najeriya dake fama da rikicin Boko Haram.