Sojojin Najeriya sun halaka ƴan bindiga a Zamfara

Sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe ‘yan fashin daji uku a wani kwanton ɓauna da suka yi musu a yankunan Anka zuwa Dan Kapani a yankin ƙaramar hukumar Anka a jihar Zamfara.

Daraktan yaɗa labarai na hukumar tsaron Manjo Janar Musa Danmadami shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar.

Manjo Janar Danmadami ya ce sojojin sun ƙwato bindiga ɗaya ƙirar PKT, da ƙirar AK- 47 guda uku tare da alburusai masu tarin yawa, da babura uku.

Sanarwar ta kara da cewa rundunar sojin ta yaba wa dakarun tare da kira ga al’umma da su riƙa bai wa jami’an sojin bayanan sirri kan ‘yan ta’addan da inda suka ayyukansu.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...