[ad_1]
An shiga rudani a filin jirgin saman Maiduguri dake jihar Borno bayan da sojoji da suka fusata suka riƙa harbin iska domin nuna kin amincewarsu da dauke su daga cikin Maiduguri.
Sojojin da suka fusata sun isa filin jirgin da misalin karfe 6:00 na yamma gabanin tura su ƙaramar hukumar Marte dake jihar.
Amma rikici ya fara ne lokacin da suka haÉ—u suka ki shiga jirgin da ya kamata ya dauke su zuwa can.
Sojojin na daga cikin soja da aka bawa horo na musamman sun bayyana cewa bayan da suka shafe shekaru huÉ—u a Maiduguri kamata ya yi a mayar da su gida wajen iyalansu amma ba a tura su inda za su fuskanci mutuwa ba.
Wani jami’i da ya sheda abinda ya faru ya ce sojojin sun gargadi manyansu da kada su zo a filin domin za su iya fuskantar harbi daga wurinsu.
[ad_2]