Sojoji sun yi bore a filin jirgin saman Maiduguri

[ad_1]








An shiga rudani a filin jirgin saman Maiduguri dake jihar Borno bayan da sojoji da suka fusata suka riƙa harbin iska domin nuna kin amincewarsu da dauke su daga cikin Maiduguri.

Sojojin da suka fusata sun isa filin jirgin da misalin karfe 6:00 na yamma gabanin tura su ƙaramar hukumar Marte dake jihar.

Amma rikici ya fara ne lokacin da suka haÉ—u suka ki shiga jirgin da ya kamata ya dauke su zuwa can.

Sojojin na daga cikin soja da aka bawa horo na musamman sun bayyana cewa bayan da suka shafe shekaru huÉ—u a Maiduguri kamata ya yi a mayar da su gida wajen iyalansu amma ba a tura su inda za su fuskanci mutuwa ba.

Wani jami’i da ya sheda abinda ya faru ya ce sojojin sun gargadi manyansu da kada su zo a filin domin za su iya fuskantar harbi daga wurinsu.




[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...