Jami’ai a arewacin Najeriya sun ce sojojin ƙasar sun kashe ’yanbindiga 45 da suka kai hari wani ƙauye a jihar Katsina.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a yammacin ranar Juma’a, kamar yadda hukumomin jihar suka tabbatar.
Tun da farko, an ce ’yanbindigar sun fito ne daga jihar Zamfara mai makwabtaka. Sun kai hari ƙauyen Alhazawa da ke ƙaramar hukumar Danmusa a ranar Alhamis. Rahotonni sun nuna cewa sun je ne domin satar shanu.
Sai dai mazauna ƙauyen sun tashi tsaye domin kare kansu. A yayin wannan artabu, sun kashe huɗu daga cikin maharan.
Bayan kwana guda da faruwar lamarin, ’yanbindigar sun sake taruwa domin ɗaukar fansa kan mazauna ƙauyen. A hanyarsu ta zuwa ƙauyen ne suka haɗu da sojojin Najeriya.
Hakan ya haifar da musayar wuta mai ƙarfi tsakanin ɓangarorin biyu. Bayanai sun ce sojojin sun kashe ’yanbindiga 45 a yayin fafatawar.
Sai dai rahotanni sun kuma ce sojoji uku sun rasa rayukansu a lokacin gumurzun.
Sojoji Sun Kqshe ’Yanbindiga 45 Bayan Harin Wani Kauye A Katsina

