Sojoji sun kashe yan ta’adda 60 a Borno

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso gabas sun kashe yan ta’adda akalla 60 a wani kazamin gumurzu da suka yi a yankin Bita a jihar Borno.

Farmakin ya fara da misalin karfe 1:09 na daren ranar Juma’a lokacin da yan ta’addar suka farma dakarun soja dake 26 Task Force Brigade.

A wani sako da ta wallafa a shafin X da aka fi sani da Twitter a baya rundunar sojan ta ce hari ta sama da kasa ya dai-daita yan ta’addar.

A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanan tsaro kan yankin tafkin Chadi ya ce dakarun sun fafata da yan ta’addar na tsawon lokaci  har ya zuwa karfe 03:23 na dare.

Ya ce rundunar sojan sama sun tura jiragen yaki na A-29 Super Tucano da kuma Dragon Platform.

Ya jiyo daga wata majiyar jami’an soja da ke cewa yan ta’adda akalla 60 aka kashe da kuma lalata wasu motoci biyu dake dauke da bindiga.

More from this stream

Recomended