
Dakarun sojan Najeriya dake karkashin rundunar samar da tsaro a jihar Plateau ta Operation Safe Haven sun kashe wasu mutane biyu da ake zargin yan bindiga ne a kusa da garin Nemaledu dake karamar hukumar Wase ta jihar.
A tabakin mai magana da yawun rundunar, Major Samson Zhakom dakarun sun kai farmakin ne biyo bayan gamsassun bayanan sirri da suka cewa anga motsin yan ta’adda a yankin.
Ya ce sojoji daga shiya ta 3 na rundunar ne suka yi kwanton bauna kusa da maboyar batagarin inda suka fafata da su a arangamar da suka yi.
Ya kara da cewa dakarun sun samu nasarar kwato bindiga AK-47 guda daya kirar gida.
Zhakom ya bayyana muhimmancin bukatar dake akwai ta hadin kan al’umma ga jami’an tsaro inda ya ce hakan zai hana batagarin samun maboya a yankin.