Sojoji sun kashe Tahir Baga kwamanda a ƙungiyar Boko Haram Tahir Baga

Dakarun  sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai sun samu nasarar kashe, Tahir  Baga wani jigo kuma kwamanda a ƙungiyar Boko Haram a cigaba da farmakin da suke kaiwa maɓoya yan ta’addar dake Dajin Sambisa.

An kashe Tahir ne a ranar 13 ga watan Mayu na shekarar 2024 a wani gagarumin farmaki da aka yiwa laƙabi  da Operation Desert Sanity III  domin kakkabe ƴan ta’addar daga Shababul Umma, Garin Panel Beater da Lagara Anguwan Gwaigwai dake tsakiyar dajin na Sambisa.

Wasu majiyoyin jami’an tsaron sirri sun faɗawa Zagazola Makama dake wallafa bayanai a kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi cewa  a lokacin  farmaki dakarun sojan sun yi arangama da ƴan ta’addar inda suka yi musu ɓarin wuta har ta kai ga sun kashe Baga da kuma wasu mabiyansa a yayin da wasunsu da dama suka tsere da raunin harbin bindiga.

Tahir Baga ya kasance makusanci ga tsohon shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau kuma yana ɗaya daga cikin mutanen farko da suka kafa kungiyar ta Boko Haram a birnin Maiduguri kafin su koma Dajin Sambisa tare da su Mamman Nur, Khalid Albarnawi, Abubakar Shekau, Kaka Ali, Mustapha Chadi, Abu Maryam da Abu Krimima.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...