
Dakarun Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa dake arewa maso gabas sun kashe akalla mayakan kungiyar yan ta’addan ISWAP/Boko Haram 20 a ciki har da kwamanda Abu Yusuf wanda shi ne Munzir na Dursula dake Goniri a karamar hukumar Gujba ta jihar Yobe.
Sojojin sun samu nasarar kashe shi ne a lokacin wasu jerin hare-hare da aka fara kai wa kan garin Goniri da daren ranar Litinin 9 ga wata har ya zuwa wayewar garin ranar Talata 10 ga watan Maris 2026.
A wata sanarwa, Laftanar Kanal Sani Uba jami’in watsa labarai na rundunar sojojin Operation Haɗin Kai ya ce yan ta’addan sun farma sojoji dake karkashin shiya ta biyu na Rundunar Operation Haɗin Kai.
Ya ce dakarun sun samu nasarar dakile farmakin yan ta’addar waɗanda su ka fito ta ƙauyen Goniri da kuma ta wajejen mahadar Ngamdu a ƙoƙarin da su ka yi na kewaye sojojin.
Ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin dakarun sojan sun jikkata amma anyi gaggawar ɗauke su ya zuwa asibiti kuma suna cikin yanayi mai kyau.

