Sojoji Sun Kashe Gawurtaccen Ɗan Bindiga Boderi

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe wasu gawurtattun masu garkuwa da mutane da suka jima suna addabar al’umma.

Mai magana da yawun rundunar sojan Najeriya, Onyeama Nwachukwu shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis .

Ya ce ƴan fashin daji shida aka kashe a yayin farmakin da aka kai a yankin Bada-Riyawa dake kan hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna a ranar 22 ga watan Faburairu.

Ya ce bayanan sirri sun bayyana cewa Boderi da Bodejo  gawurtattun masu garkuwa da mutane na daga cikin yan fashin dajin da aka kashe a yayin arangamar.

Mutanen biyu sune ke da alhakin kai hari kan makarantar sojoji ta NDA,  kwalejin aikin gona dake Afaka, jami’ar Greenfield da kuma makarantar ƴan mata ta Yauri.

Baderi ya shafe shekaru da dama yana addabar al’umma kana ana zarginsa da haɗa baki da ƴan ta’adda domin kafa masu sansani a dazukan dake yankunan da yake da iko da su.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...