Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso gabashin Najeriya sun samu nasarar kai wani harin kwanton ɓauna kan mayaƙan Boko Haram inda suka kashe mutum guda tare da jikkata wasu da dama.

Dakarun sun kai harin ne a kusa da garin Darel Jamel dake ƙaramar hukumar Bama ta jihar Borno.

Wata majiyar jami’an tsaron sirri ta faɗawa Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro kan yankin tafkin Chadi cewa an kai harin kwanton ɓaunar ne a ranar 13 ga watan  Oktoba biyo bayan bayanan sirri da dakarun suka samu kan ayyukan ƴan ta’addan.

A yayin farmakin sojojin sun samu nasarar samun harsashi da dama.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

TCN na ci gaba da ƙoƙarin gyaran wutar lantarkin da ta lalace kwana biyu

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya sanar da ci gaban da aka samu wajen farfado da rukunin wutar kasa bayan wata tangardar...