Sojoji sun kashe É—an bindiga a Kaduna

Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta sun kashe yan bindiga da kuma gano bindigar AK-47 É—aya a Kaduna.

Jami’an sojojin rundunar shiya ta É—aya ne suka kai farmakin a kananan hukumomin Chikun da Kajuru.

Musa Yahaya mai rikon muÆ™amin jami’in hulÉ—a da jama’a na rundunar sojan Najeriya shiya ta É—aya shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa ranar Laraba.

Ya ce sojojin bisa dogaro da bayanan sirri sun yi kwanton ɓauna a kan hanyar da ƴan bindigar suke bi a titin Kwant-Kabai-Kubusu a ranar Laraba.

Yahaya ya ce farmakin wani bangare ne na Æ™oÆ™arin da rundunar take na raba jihar da Æ´an ta’ada, Æ´an bindiga da kuma sauran batagari dake dazukan jihar.

Ya ce a yayin farmakin a musayar wutar da aka yi É—an bindiga guda ya rasa ransa yayin da sauran suka tsere da raunin harbin bindiga.

“bindigar AK-47 guda É—aya, gidan harsashi É—aya, maganin dabbobi da kuma kayan sawa su ne aka gano” a cewar sanarwar.

More News

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama Æ´an kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan Æ´an sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan Æ´an...

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto. Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da...

Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman. Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake...