
Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta sun kashe yan bindiga da kuma gano bindigar AK-47 É—aya a Kaduna.
Jami’an sojojin rundunar shiya ta É—aya ne suka kai farmakin a kananan hukumomin Chikun da Kajuru.
Musa Yahaya mai rikon muÆ™amin jami’in hulÉ—a da jama’a na rundunar sojan Najeriya shiya ta É—aya shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa ranar Laraba.
Ya ce sojojin bisa dogaro da bayanan sirri sun yi kwanton ɓauna a kan hanyar da ƴan bindigar suke bi a titin Kwant-Kabai-Kubusu a ranar Laraba.
Yahaya ya ce farmakin wani bangare ne na Æ™oÆ™arin da rundunar take na raba jihar da Æ´an ta’ada, Æ´an bindiga da kuma sauran batagari dake dazukan jihar.
Ya ce a yayin farmakin a musayar wutar da aka yi É—an bindiga guda ya rasa ransa yayin da sauran suka tsere da raunin harbin bindiga.
“bindigar AK-47 guda É—aya, gidan harsashi É—aya, maganin dabbobi da kuma kayan sawa su ne aka gano” a cewar sanarwar.