Sojoji sun kashe ƴan ta’adda biyu tare da gano makamai a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe wasu ƴan ta’adda biyu a ƙauyen Kana dake ƙaramar hukumar Biu ta jihar Borno.

A wata sanarwa ranar Asabar rundunar sojan ta ce an kashe ƴan ta’addar ne a ranar 19 ga watan Afrilu.

Rundunar sojan ta ce dakarunta sun yi arangama da ƴan ta’addar a wajejen ƙauyen Nguma ta kara da cewa an gano babur ɗaya da kekuna 6 sai bindiga ƙirar AK-47 da kuma sauran kayayyaki da aka yi watsi da su.

A kuma wani samamen na daban dakarun sojan na Najeriya sun kai samame a ƙauyen Abuni dake ƙaramar hukumar Awe ta jihar Nasarawa kan wasu maɓoyar bata gari inda aka gano bindigogi.

An samu nasarar gano bindigogi biyu ƙirar AK-47 a gidan wani da ake kira Abdullahi Musa tare da kama ƙarin wasu mutane.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...