Sojoji sun kashe ƴan fashin daji 5 a Kaduna

Dakarun rundunar Operation Whirl Punch dake aikin samar  da tsaro a jihar Kaduna sun kashe wasu mutane biyu da ake zargin ƴan fashin daji ne.

A wata sanarwa ranar Litinin, Samuel Aruwan kwamishinan  tsaro da harkokin cikin gida ya ce an tare waɗanda  ake zargin ne a ƙaramar hukumar Kajuru dake jihar.

Aruwan ya ce sojojin sun ƙwace bindigar AK-47 guda biyu, bindigar mashin gan ƙirar gida, gidan zuba harsashin AK-47 guda 9, har sashi 250, babura guda biyu sai kuma rediyo guda biyu.

Sanarwar ta ce sojojin sun yi arangama da ƴan bindigar a ƙauyen Ɗantarau nan take aka kashe biyar daga cikinsu bayan musayar wuta tsakaninsu da jami’an tsaro.

Ya ƙara da cewa wasu daga cikin ƴan bindigar sun tsere da raunin harbin bindiga inda ya shawarci jama’ar yankin da suka idanu sosai kuma kada su sake su taimakawa ƴan bindigar da ka iya zuwa neman magani.

Tuni gwamnan jihar Mallam Uba Sani ya yabawa jami’an tsaron kan ƙoƙarinsu na inganta tsaro a jihar.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...