Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga Biyu Tare Da Ceto Mutane 20 Da Aka Yi Garkuwa Dasu A Jihar Zamfara

Dakarun Rundunar Sojan Najeriya sun kashe ƴan fashin daji biyu ciki har da wani gawurtaccen ɗan bindiga a jihar Zamfara.

A wata sanarwa ranar Talata, Yahaya Ibrahim jami’in yaɗa labarai na rundunar Operation Hadarin Daji ya ce an kashe ƴan ta’addar ne a wani farmaki da aka kai maɓoyarsu dake kananan hukumomin Zurmi da Birnin Magaji a jihar Zamfara.

Ibrahim ya ce sojojin sun ceto mutane 20 da aka yi garkuwa da su da suka haɗa da mata da kuma ƙananan yara.

Ya ce sojojin sun samu nasarar lalata maɓoyar yan ta’addar da kuma maɓoyar wani fitaccen ɗan bindiga da ake kira Sule.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...