
Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 6 lokacin da suke sintiri a yankin ƙananan hukumomin Birnin Gwari da Giwa a jihar Kaduna.
Samuel Aruwan kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida shi ne ya bayyana haka inda ya ce sojojin sun samu makamai da harsashi da suka haÉ—a da bindigar AK-47 guda biyu gidan harshi guda 4, yunifam É—in yan ta’addar na mutum 40 da kuma baburan hawa 9.
Sanarwar ta ce sojojin sun yi arangama da Æ´an bindigar ne a yankin Mindaro, Kidandan da kuma Ngade.
Aruwan ya ce gwamnan jihar, Uba Sani ya ya yaba tare da jin É—aÉ—in labarin kisan yan bindigar.