Sojoji sun kama wani hatsabibin barawo mai garkuwa da mutane a jihar Zamfara

[ad_1]








Sojojin Najeriya da suka fito daga Rundunar Sojan Najeriya Shiya ta Daya, sun kashe wasu barayi biyar ciki har da kasurgumin barawon nan da ake kira da Sani Danbuzuwa da ya fito daga jihar Zamfara.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar a Kaduna mai dauke da sahannun jami’in hulda hulda da jama’a na shiryar, Kanal Muhammad Dole.

Ya ce soja daya ya mutu lokacin da suka rufafa yan fashin ya zuwa cikin dajin Kwuyambana dake jihar Zamfara ya yin da wasu biyu kuma suka jikkata ya kara da cewa “Wadanda suka jikkata an dauke su ya zuwa asibitin asibitin sojoji sojojin dake Kaduna kuma suna murmurewa.”

“Sojojin sun amsa kiran kai daukin gaggawa akan ana aikata fashi da makami akan hanyar Birnin Gwari zuwa Funtua inda wasu da ake zargin barayin ne sukai musu kwanton bauna.

“Amma sun samu nasarar fin ƙarfin barayin hakan ya sa suka gudu cikin dajin Kwuyambana dake jihar Zamfara.”

Sanarwar ta kara da cewa sojojin ranar 14 ga watan Agusta sun kama wani hatsabibin mai garkuwa da mutane a kauyen Sambuwa mai suna,Yinusa Sulaiman da ya kware wajen tattauna biyan kudin fansa.

Har ila yau sojojin sun samu nasarar gano bindigogi da dama a wurin da aka yi artabun.




[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...