Sojoji sun kama wanda ake zargi ya kashe sabbin ma’aurata a Filato

Sojojin Najeriya karkashin Operation Safe Haven, OPSH, ta cafke wani da ake zargin ya kashe wasu ma’aurata a kauyen Kwi da ke karamar hukumar Riyom a jihar Filato.

Lt.-Kol. Ishaku Takwa, Mukaddashin Daraktan Hulda da Jama’a na Runduna ta 3 ta Sojojin Najeriya, Rukuba, kusa da Jos, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai ranar Asabar a Jos.

Idan ba a manta ba a ranar 14 ga watan Agusta, wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kashe wasu sabbin ma’aurata, daya mai suna Rwang Danladi mai shekaru 37 da matarsa, Sandra mai shekaru 28.

Ma’auratan, dukkansu malaman sakandaren BECO Comprehensive Secondary School, da ke Kwi, an kashe su ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari a makarantar.

Mista Takwa ya bayyana cewa an kama wanda ake zargin ne a ranar 18 ga watan Nuwamba a unguwar Tafawa da ke Barkin Ladi, biyo bayan jajircewar da sojojin suka yi.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...