Sojoji sun kama masu yi wa Boko Haram leken asiri a Borno 

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai dake yaƙi da yan ta’adda a yankin arewa maso gabas sun kama wasu mutane biyu da ake zargin masu leken asirine na  mayakan kungiyar Boko Haram/ISWAP a karamar hukumar Damboa ta jihar Borno.

Da yake magana da Zagazola Makama wanda ke wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi wata majiyar jami’an tsaro ta bayyana cewa waɗanda aka kama sun haɗa da Musa Alhaji Isa mai shekaru 28 da kuma Alhaji Akona an kama su ne a ranar 23 ga watan Maris a lokacin da jami’an tsaro su ke aikin wani samame da suka saba yi.

“Mutanen dukkansu sun fito daga garin Shawari dake ƙaramar hukumar Damboa an tsare su ne a yankin da ake kira Serial 7 inda ya haɗa da yankin Timbuktu da ya yi kaurin suna wajen tara yan ta’adda,” a cewar majiyar.

Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa mutanen suna leken asiri ne inda su ke tattara bayanai domin mikawa yan ta’addan dake yankin.

Kayayyakin da aka samu a tare da su sun haɗa da keken hawa biyu, wayoyin hannu, tocilan, agogon hannu da kuma kuɗi har naira 6900.

More from this stream

Recomended