
Dakarun rundunar sojan Najeriya na shiya ta 6 sun samu nasara kama mutane 43 da ake zargin suna da hannu a gudanar da wasu haramtattun matatun man fetur a yankin Neja Delta.
Danjuma Danjuma mai riƙon muƙamin mataimakin daraktan hulɗa da ƴan jaridu na rundunar ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a Fatakwal babban birnin jihar Rivers.
Danjuma ya bayyana cewa an kama mutanen a tsakanin ranakun 31 ga watan Maris ya zuwa 06 ga watan Afrilu a jihohin Beyalsa Delta da kuma Ribas.
Ya ƙara da cewa sojojin sun lalata haramtattun matatun mai 14 kwace jiragen ruwa 14 da kuma kwace lita 254,000 na nau’ikan manfetur iri-iri da aka sata.
Fasa bututun mai tare dan satar mai abu ne da ya zama ruwan dare a yankin Neja Delta dake da dimbin arzikin duk da irin wannan kamen da jami’an tsaro suke yi za a iya cewa hukumomin sun gaza wajen kawo ƙarshen lamarin.