Sojoji sun ‘halaka ‘yan fashi 135’ a Katsina da Zamfara

Sojojin Najeriya

Hakkin mallakar hoto
Nigerian Army

Image caption

Rundunar sojan Najeriya ta ce ta lalata sansanoninsu da dama

Dakarun rundunar Hadarin Daji ta sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe ‘yan fashi 135 a wani hari ta sama a jihohin Kastina da Zamfara cikin kwana biyu.

A wata sanarwa da jami’in tattara bayanai na hedikwatar tsaro da ke Abuja, Manjo Janar John Enenche, ya fitar ranar Asabar ta ce an kai hare-haren ne a ranakun Laraba 20 ga watan Mayu zuwa Juma’a 22, inda ta lalata sansanoninsu.

Daga cikin sansanonin da aka hara akwai Sansanin Abu Radde na ɗaya da na biyu, da kuma Dunya da ke ƙananan hukumomin Jibya da Ɗan Musa dukansu a Jihar Katsina, a cewar rundunar.

Sauran sun haɗa da Sansanin Hassan Tagwaye da Sansanin Maikomi da ke ƙananan hukumomin Birnin Magaji da kuma Zurmi na Jihar Zamfara.

Wannan nasara da rundunar ta yi ikirari na zuwa ne mako É—aya bayan umarnin da Shugaba Muhammadu ya bayar na kakkaÉ“e ‘yan fashi daga jihohin na Katsina – jihar da ya fito – da kuma Zamfara.

Kungiya mai bincike kan tashe-tashen hankula a ƙasashen duniya, International Crisis Group, ta ce an kashe mutum fiye da 8,000 a rikicin arewa maso yammacin ƙasar cikin shekara 10.

Kungiyar ta ce rikicin ya raba fiye da dubu É—ari 200 da muhallansu a rikice-rikice da kuma hare-hare a yankin.

A baya-bayan nan rundunar ta sha ikirarin samun nasara a kan ‘yan bindiga, sai dai babu wata kafa mai zaman kanta da take tabbatar da rahotannin.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...