Sojoji sun ‘halaka ‘yan fashi 135’ a Katsina da Zamfara

Sojojin Najeriya

Hakkin mallakar hoto
Nigerian Army

Image caption

Rundunar sojan Najeriya ta ce ta lalata sansanoninsu da dama

Dakarun rundunar Hadarin Daji ta sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe ‘yan fashi 135 a wani hari ta sama a jihohin Kastina da Zamfara cikin kwana biyu.

A wata sanarwa da jami’in tattara bayanai na hedikwatar tsaro da ke Abuja, Manjo Janar John Enenche, ya fitar ranar Asabar ta ce an kai hare-haren ne a ranakun Laraba 20 ga watan Mayu zuwa Juma’a 22, inda ta lalata sansanoninsu.

Daga cikin sansanonin da aka hara akwai Sansanin Abu Radde na ɗaya da na biyu, da kuma Dunya da ke ƙananan hukumomin Jibya da Ɗan Musa dukansu a Jihar Katsina, a cewar rundunar.

Sauran sun haɗa da Sansanin Hassan Tagwaye da Sansanin Maikomi da ke ƙananan hukumomin Birnin Magaji da kuma Zurmi na Jihar Zamfara.

Wannan nasara da rundunar ta yi ikirari na zuwa ne mako É—aya bayan umarnin da Shugaba Muhammadu ya bayar na kakkaÉ“e ‘yan fashi daga jihohin na Katsina – jihar da ya fito – da kuma Zamfara.

Kungiya mai bincike kan tashe-tashen hankula a ƙasashen duniya, International Crisis Group, ta ce an kashe mutum fiye da 8,000 a rikicin arewa maso yammacin ƙasar cikin shekara 10.

Kungiyar ta ce rikicin ya raba fiye da dubu É—ari 200 da muhallansu a rikice-rikice da kuma hare-hare a yankin.

A baya-bayan nan rundunar ta sha ikirarin samun nasara a kan ‘yan bindiga, sai dai babu wata kafa mai zaman kanta da take tabbatar da rahotannin.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...