
Dakarun rundunar sojan Najeriya sun samu nasarar dakile wani farmaki da ake zargin mayakan kungiyar yan ta’addan ISWAPÂ da kai wa kan wani sansanin soja dake Doron Baga a karamar hukumar Kukawa ta jihar Borno.
A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi yan ta’addan sun kai farmaki sansanin sojan da misalin karfe 02:12 na daren ranar Talata abun dai ya haifar da musayar wuta ta tsawon mintuna 55.
Makama ya bayyana cewa dakarun sojan sun nuna dagiya kwarewa da Ć™wazo a fafatawar da aka aka yi da Ć´an ta’addan .
Wata majiyar jami’an tsaro ta bayyana cewa yan ta’adda da dama dakarun sojan su ka kashe a yayin arangamar tare da kwace makamai masu tarin yawa.
A ɓangaren sojojin ba a samu asarar rayuka ba da kuma na kayan aiki.

