Rundunar Sojan Najeriya Shiya ta 1 ta ce dakarunta sun ceto mutane 6 da aka yi garkuwa da su a yayin da aka kashe É—an bindiga guda É—aya a musayar wuta.
Mai rikon muÆ™amin darakta hulda da jama’a na Rundunar Sojan Najeriya Shiya ta 1 dake Kaduna, Kanal Musa Yahaya wanda ya tabbatar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar a Kaduna ya ce an ceto mutanen ne a ranar Juma’a.
Yahaya ya ce cigaba da kakkabe yan bindiga daga maboyarsu na haifar da mai ido.
Ya ce rundunar ta yi amfani da bayanan da ta samu cewa wasu yan bindiga sun sace mutane 6 a yankin Hayin Tsando na Maraban Jos a karamar hukumar Igabi ta jihar.
Sojoji sun hanzarta kaddamar bincike tare da kokarin ceto mutane har ta kai ga sun yi musayar wuta da yan bindiga.
“A lokacin arangamar sojoji sun ceto mutane 6 da aka yi garkuwa da su samun bindigar AK-47 guda biyu tare kashe É—an bindiga É—aya a yayin da sauran suka tsere da raunin harbin bindiga,” a cewar sanarwar.