Akalla yan ta’adda 22 aka rawaito an kashe a wani harin da sojan saman Najeriya suka kai musu a jihar Borno.
A wata sanarwa ranar Litinin mai magana da yawun rundunar sojan Najeriya, Edward Gabkwet ya ce an kashe yan ta’addar ne a ranar Lahadi a wata matartararsu a kokarin da suke na boyewa bin sahunsu da sojoji suke.
Gabkwet ya ce an kai harin ne biyo bayan bayanan sirri da suka samu dake nuna cewa ƙalla yan ta’adda 22 aka gani a motoci masu ɗauke da bindiga da kuma babura biyu a kusa da Marte.
Ya ce hakan yasa aka yi gaggawar tura jirgin yaƙin sojan Najeriya kuma ya gano yan ta’addar a nisan tazarar kilomita 22 yammacin Marte inda suka nufi arewa wajen Monguno.