Soja daya da kuma wasu mutane 9 sun mutu a ambaliyar ruwa a jihar Kebbi.

[ad_1]








Gwamnatin jihar Kebbi a ranar Talata ta tabbatar da mutuwar wani soja guda daya da kuma wasu mutane 9 a wata ambaliyar ruwa biyu da aka yi a jihar.

A wata sanarwa da aka fitar a birnin Kebbi mai dauke da sahannun, Abubukar Dakingari jami’in yada labaran gwamnan jihar, Atiku Bagudu, ya ce ambaliyar ruwan ta faru a kananan hukumomi biyu dake jihar.

Dakingari ya lissafa kauyukan da abin ya shafa da suka hada da kauyen Kanya a karamar hukumar Danko Wasagu da kuma kauyen Mahuta a karamar hukumar Fakai.

Ya ce ” wani soja da kuma wasu mutane sun rasa rayukansu a mamakon ambaliyar ruwa sakamakon yawan ruwan sama a jihar an ce sojan ya mutu ne lokacin da yake kokarin ceto wata mace daga ambaliyar ruwan.

Dakin gari ya ce duk da an samu nasarar samun gawar matar amma ruwa ya tafi da gawar sojan.

Ya kara da cewa mutane biyar ne suka mutu a kauyen Kanya, uku kuma a Mahuta.




[ad_2]

More News

Ƴan sanda sun kama masu sayen kuri’a a zaben gwamnan Edo

Jami'an rundunar ƴan sandan Najeriya sun kama wasu mutane 9 da ake zarginsu da sayen kuri'a da kuma mallakar kuri'ar da aka riga aka...

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...