Shugabannin kasashen duniya sun mika sakonnin yabo ga marigayi Kofi Annan, daya daga cikin ‘yan Afirka da suka shahara, a lokacin binne shi da aka yi a kasarsa ta Ghana.
Wannan ne karshen kwanaki uku na zaman makoki da gwamnatin kasar ta ayyana, kuma dubban ‘yan kasar sun ziyarci babban dakin taro na birnin Accra inda aka ajiye gawarsa domin nuna jimaminsu.
Mista Annan ya mutu a ranar 18 ga watan Agusta yana da shekara 80 da haihuwa.
Ya zama babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya daga 1997 zuwa 2006, kuma shi ne bakar fata na farko da ya taba rike wannan babban mukamin na diflomasiyya.
An kuma ba shi lambar yabo ta Nobel a 2001 saboda rawar da ya taka ta inganta ayyukan majalisar, a lokacin da ake yakin Iraki da ake kuma fama da annobar cutar AIDS ko SIDA.
A wajen bikin, babban sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya mai ci, Antonio Guterres ya ce Mista Annan ya kasance mutumin da ya mayar da majalisar ta zama mai taimaka wa wajen rage fitunu a duniya.
Wadanda suka halarci bikin sun sanya kaya masu launin baki da ja, kuma sun cika babban dakin taro na Accra mai daukan mutum 4,000.
Wasu kuma sun kalli bikin ne a wasu manyan allunan talabijin da aka kafa musamman domin nuna wa jama’a kai tsaye yadda al’amura ke gudana.
Kojo Amoo-Gottfried wanda dan dan uwan Mista Kofi Annan ne, ya karanta sakon karrama wa a lokacin bikin, inda ya bayyana cewa Mista Annan ya yi jagorancin boren kin cin abinci a lokacin yana dan makaranta domin yadda ake ba wa ‘yan makaranta abinci maras kyau.
Tshuwar sarauniyar kasar Holland Gimniya Beatrix na daga cikin wadanda suka halarci zaman makokin tare da matar danta Gimbiya Mabel. Dukkansu aminan Mista Annan ne.
Sarkin Asante Otumfuo Nana Osei Tutu II, ya nada wa Mista Annan sarautar “Busumuru” a 2012 domin karrama ayyukan da ya yi na diflomasiyya a duniya.
Basumuru sunan daya daga cikin takubban da ke makale a karagar zinare ta masarautar Asante.
Shugaban Ghana Nana Akufo-Addo ya bayyana Mista Annan a matsayin “daya daga cikin shararrun mutanen wannan karnin da muke ciki”.
Babban limamin cocin Anglika na Kumasi, wanda shi ne asalin garin da Mista Annan ya fito, Rabran Daniel Sarfo ya ce: “Yau rana ce da aka kafa tarihi a nan Ghana. Daya daga cikin shahararrun ‘ya’yanmu ne ke kwance a nan.”
Amma muna matukar farin ciki cewa ubangiji ya yi amfani da shi wajen gudanar da ayyukan da suka inganta rayuwar dan Adam, da samar da zaman lafiya. A yau aikinsa ya kammala.”
Dukkan hotunan nan na da hakkin mallaka akansu.