Shugabannin kananan hukumomin Bayelsa sun fice daga jam’iyar PDP

Shugabannin kananan hukumomi shida sun bayyana goyon bayansu ga gwamnan jihar Bayelsa, Douye Diri kan sauya shekar da ya yi zuwa jam’iyar APC daga PDP.

A ranar Laraba gwamnan ya sanar da ficewarsa daga jam’iyar adawa ta PDP saboda wasu dalilai da ya ce bayyanannu a fili.

Diri ya kara da cewa mambobin majalisar zartarwa ta jihar da kuma yan majalisar dokoki ta jihar sun fice daga jam’iyar ta PDP a tare da shi.

Biyo bayan haka ne su ma shugabannin Æ™ananan hukumomi Æ™arÆ™ashin kungiyar ALGON suka sanar da fitarsu daga jam’iyar PDP a wani taron manema labarai da suka yi a ginin sakatariyar kungiyar dake birnin Y

Lelei Tariye Isaac, shugaban karamar hukumar Kolokuma/Opokuma wanda ya yi magana a matsayin shugabannin kananan hukumomin ya ce sun dauki matakin saboda rikicin da ya dabaibaye jam’iyar ta PDP.

More from this stream

Recomended