Fadar Shugaban Ƙasa ta karɓi cikakken rahoton tsaro daga Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, dangane da harin ta’addanci da aka kai a ƙaramar hukumar Kaiama.
Ganawar ta gudana ne a ranar Alhamis a fadar gwamnati da ke Abuja, bayan mummunan harin da aka kai wa al’ummomi, musamman a ƙauyen Woro, inda rahotanni suka ce ‘yan ta’adda sun farmaki mazauna da suka ƙi amincewa da koyarwar tsattsauran ra’ayi.
Rahotannin farko sun nuna cewa akalla mutane 75 ne suka rasa rayukansu. Sai dai sabbin bayanai sun nuna cewa adadin ya ƙaru zuwa kusan mutane 162.
Gwamna AbdulRazaq, wanda ya ziyarci yankunan da abin ya shafa tare da jami’an tsaro a ranar Laraba, ya bayyana harin a matsayin “ainihin kisan gilla”, tare da umartar hukumar agajin gaggawa ta jihar da ta gaggauta kai tallafin jin ƙai ga waɗanda abin ya shafa.
A martanin da ya mayar kan lamarin, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da tura rundunar sojoji ta bataliya zuwa Kaiama. Haka kuma ya sanar da ƙaddamar da wani sabon shirin soja mai suna “Operation Savannah Shield,” domin murƙushe ‘yan ta’addan da kuma kare al’ummomin da ke cikin haɗari.
Shugaba Tinubu Ya Karɓi Rahoton Tsaro Daga Gwamnan Kwara Kan Harin Ta’addanci

