Eng Babacir ya kara da cewa idan jam’iyyar APC bata yi takatsantsan ba, za ta iya rasa jihar Adamawa a zaben 2019. Yanzu haka mutane hudu sun sayi fom din tsayawa takarar Gwamna a jam’iyyar APC a Adamawa, yana mai cewa idan aka hana uku tsayawa takara hakan zai iya janyo wasu su ki yiwa jam’iyya aiki ko su balle.
Da wakilin sashen Hausa ya tambaye shi ko shin yana neman tsayawa takara ne? Sai ya ce ‘’A’A, na tsufa na fi shekarun gwamna’, Ya kara da cewa ba ya neman komai. Ya ce idan uwar jam’iyya ba ta yarda da bukatarsu ba za su fita su zabi shugaba Muhamadu Buhari amma ba za su zabi gwamna ba. Babacir ya ce banda aikin kama karya da gwamnan jihar Adamawa ya yi, bai yi wani aiki na a zo a gani ba.
Da yake mayar da martani kan wannan batu, kwamishinan labarai na jihar Adamawa Sir. Joe Ahmed, ya ce dokar tsarin mulkin jam’iyyar APC ce ta fida hanyoyin da za bi a fida gwanaye. Ya ce shuwagabanin jam’iyyar ce ta dauki wannan matsayin ‘yar tinke. Ya kara da cewa kiyyaya da hassada ce za ta sa mutum ya shiga jihar Adamawa ya ce bai ga komai a kasa ba.