Shin APC Za Ta Amince Da Zaben Yar Tinke A Jihar Adamawa

Eng Babacir ya kara da cewa idan jam’iyyar APC bata yi takatsantsan ba, za ta iya rasa jihar Adamawa a zaben 2019. Yanzu haka mutane hudu sun sayi fom din tsayawa takarar Gwamna a jam’iyyar APC a Adamawa, yana mai cewa idan aka hana uku tsayawa takara hakan zai iya janyo wasu su ki yiwa jam’iyya aiki ko su balle.

Da wakilin sashen Hausa ya tambaye shi ko shin yana neman tsayawa takara ne? Sai ya ce ‘’A’A, na tsufa na fi shekarun gwamna’, Ya kara da cewa ba ya neman komai. Ya ce idan uwar jam’iyya ba ta yarda da bukatarsu ba za su fita su zabi shugaba Muhamadu Buhari amma ba za su zabi gwamna ba. Babacir ya ce banda aikin kama karya da gwamnan jihar Adamawa ya yi, bai yi wani aiki na a zo a gani ba.

Da yake mayar da martani kan wannan batu, kwamishinan labarai na jihar Adamawa Sir. Joe Ahmed, ya ce dokar tsarin mulkin jam’iyyar APC ce ta fida hanyoyin da za bi a fida gwanaye. Ya ce shuwagabanin jam’iyyar ce ta dauki wannan matsayin ‘yar tinke. Ya kara da cewa kiyyaya da hassada ce za ta sa mutum ya shiga jihar Adamawa ya ce bai ga komai a kasa ba.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...