Sanata mai wakiltar mazabar, Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani a ranar Asabar ya sayi fom din takarar kujerar sanata karkashin jam’iyar APC.
Sanatan ya sayi fom din takarar a sakatariyar jam’iyar APC dake Abuja cikin dandazon magoya baya.
Ya samu rakiyar magoya bayansa da suka fito daga kananan hukumomi 7 na mazabar.
Da yakewa magoya bayansa jawabi gabanin sayan fom din takarar, Sani ya yi alkawarin cigaba da wakilci nagari inda ya gode musu kan gagarumin goyan bayan da suke bashi.
Ya kuma yi alkawarin cewa bazai basu kunya ba, kana ya kuma jaddada muhimmancin yin zaben fidda gwani na kai tsaye.
Takarar ta Shehu Sani na zuwa ne duk da takun sakar dake tsakaninsa da gwamnan jihar, Malam Nasiru El-rufa’i.