Shehu Sani ya sayi fom din takara

Sanata mai wakiltar mazabar, Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani a ranar Asabar ya sayi fom din takarar kujerar sanata karkashin jam’iyar APC.

Sanatan ya sayi fom din takarar a sakatariyar jam’iyar APC dake Abuja cikin dandazon magoya baya.

Ya samu rakiyar magoya bayansa da suka fito daga kananan hukumomi 7 na mazabar.

Da yakewa magoya bayansa jawabi gabanin sayan fom din takarar, Sani ya yi alkawarin cigaba da wakilci nagari inda ya gode musu kan gagarumin goyan bayan da suke bashi.

Ya kuma yi alkawarin cewa bazai basu kunya ba, kana ya kuma jaddada muhimmancin yin zaben fidda gwani na kai tsaye.

Takarar ta Shehu Sani na zuwa ne duk da takun sakar dake tsakaninsa da gwamnan jihar, Malam Nasiru El-rufa’i.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...