Sharhin Masana Kan Batun Girke Jami’an Tsaro a Majalisar Dokokin Najeriya

[ad_1]

Masu sharhin sun bayyana cewa tun farko yadda aka kirkiro jam’iyyar APC daga jam’iyyu masu bambancin ra’ayi da kuma akida ya taimaka wajen rashin iya tafiyar da ayyukan gwamnati a siyasance.

Malam Zailani Baffa na Jami’ar Tafawa Balewa dake Bauchi, na ganin cewa salon da shuba Buhari ya dauka na kyale kowa yayi yadda ya ga dama shi ya samar da kafar da kadangare ya shiga.

Shi kuma malam Yusuf Abdullahi, na kwalejin kimiya da fasaha ya ce hadakar da aka yi tsakanin jam’iyyun a APC tun farko a jam’iyyar bai yi daidai ba saboda akidun su sun bambanta. Ya kara da cewa matakin kai jami’an tsaro na DSS majalisar bai dace ba, kuma idan aka yi la’akari za a ga cewa a lokacin da jami’an tsaron suka toshe ginin majalisar ‘yan PDP ne kawai a wajen.

A nasa tsokacin shugaban kungiyar wanzar da zaman lafiya tsakanin musulmai da kristoci, Ambasada Aminu Garba sidi, matakin da mukaddashin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya dauka ya kare martabar dimokradiyya.

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...