Sha’anin tsaro na ƙara inganta a jihar Borno – Zulum

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya ce an samu ingantuwar tsaro a jihar ya kai matakin kaso 85 cikin 100.

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Juma’a lokacin da yake magana da yan jaridar dake fadar shugaban kasa bayan wata ganawa da yayi da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Zulum ya jinjinawa rundunar sojan Najeriya, yan sanda, hukumomin tsaro da rundunar sojan sama inda ya bayyana yadda hukumomin ke aiki tare wajen samar da tsaro a jihar.

Ya kuma ya bawa manyan hafsoshin rundunar sojan Najeriya da kuma shugaban kan kokarin na samar tsaro.

Kalaman na gwamna Zulum na zuwa ne biyo bayan rahoton da wasu kafafen yaɗa labarai suka wallafa cewar ana samun karuwar matsalar tsaro a jihar ta Borno.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...