Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya ce an samu ingantuwar tsaro a jihar ya kai matakin kaso 85 cikin 100.
Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Juma’a lokacin da yake magana da yan jaridar dake fadar shugaban kasa bayan wata ganawa da yayi da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
Zulum ya jinjinawa rundunar sojan Najeriya, yan sanda, hukumomin tsaro da rundunar sojan sama inda ya bayyana yadda hukumomin ke aiki tare wajen samar da tsaro a jihar.
Ya kuma ya bawa manyan hafsoshin rundunar sojan Najeriya da kuma shugaban kan kokarin na samar tsaro.
Kalaman na gwamna Zulum na zuwa ne biyo bayan rahoton da wasu kafafen yaɗa labarai suka wallafa cewar ana samun karuwar matsalar tsaro a jihar ta Borno.