Sauyin Sheka Ya Sa An Kori Dan Majalisar Jiha a Neja

[ad_1]

Majalisar dokokin jihar Neja ta ce ta dauki wannan mataki ne saboda dan majalisar ya canza sheka daga APC mai Mulki zuwa Jam’iyyar Adawa ta PDP kuma ta ayyana kujerarsa a matsayin wadda babu kowa akanta.

Shugaban majalisar Dokokin jihar Neja Hon. Ahmad Marafa Guni, a wata hira ta waya da wakilin sashen Hausa Mustapha Nasiru Batsari, ya ce uwar jam’iyyarsu ta APC ce ta kawo korafi akan dan Majalisar da ya canza sheka shi ya sa suka dauki matakin.

To amma dan majalisar da aka kora Hon. Danladi Iya yace zai je kotu domin kalubalantar wannan matakin. Hakazalika shima shugaban Marasa rinjaye a majalisar, Hon. Bello Agwara yace Majalisar tayi saurin daukar Matakin korar, ya kara da cewa kamata yayi abi doka.

Kokarin jin ta bakin shugabannin Jam’iyyar ta APC a jihar Neja ya ci tura, sai dai mai taimakawa gwamnan jihar Neja akan harkokin Majalisar Wanda kuma jigo ne a jam’iyyar APC, Hon. Abdulhamed El’wazir yace majalisar tayi aikinta ne.

Saurari cikakken rahoton Mustapha Nasiru Batsari

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...