Sarkin Bauchi Ya Dauki Nauyin Karatun Wasu Marayu Da Marasa Karfi

A cigaba da manufofin sa na ganin harkokin ilimi na bunkasa,musamman ma mata da matasa masu hali da talakawa sun samu ilimi a kasar Bauchi, Mai Martaba Sarkin Bauchi Injiniya Alh Dr Rilwanu Sulaiman Adamu, ya dauki dawainiyar wasu Yara marayu da kuma ya’yan mutane marasa karfi cikin al’umma. Inda Mai martaba Sarkin Bauchi, ya saya musu dukkanin kayan da dan makaranta ke bukata domun neman ilimi cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.

Mai Martaba Sarkin Bauchi ya dinka wa yaran kayan makaranta, an saya musu littatafai, takalma, Jakunkunan makaranta kamar yadda kowane uba ke yi wa ya’yansa.

Yaran za su ci gaba da gudanar da karatun su ne karkashin kulawar Mai Martaba Sarkin Bauchi, inda zai ci gaba da daukar nauyin karatun su daga makarantan firamare yanzu har matakin karatu na gaba.

Hotuna Daga Nasiru Muazu

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...