
Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa kuma shugaban darikar Kwankwasiya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi wata ganawar sirri da sakataren jam’iyar ADC na ƙasa, Rauf Aregbesola a Abuja a ranar Alhamis.
Babu wani cikakken bayani da ya fito kan abinda ganawar ta mayar da hankali a kai amma dai Kwankwaso ya tabbatar da cewa ganawar ta gudana a gidansa a gidansa dake Abuja.
Sakon da Kwankwaso ya wallafa a shafinsa na Facebook ya bayyana cewa ya yi farin cikin karbar bakuncin a Aregbesola a gidansa dake Abuja.
A yan kwanakin nan dai ana cigaba da raɗe-raɗin cewa jagoran jam’iyar ta NNPP na duba yiyuwar shiga jam’iyar adawa ta APC tare da magoya bayansa.

