Sakataren jam’iyyar ADC na ƙasa ya ziyarci Kwankwaso

Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa kuma shugaban darikar Kwankwasiya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi wata ganawar sirri da sakataren jam’iyar ADC na ƙasa, Rauf Aregbesola a Abuja a ranar Alhamis.

Babu wani cikakken bayani da ya fito kan abinda ganawar ta mayar da hankali a kai amma dai Kwankwaso ya tabbatar da cewa ganawar ta gudana a gidansa a gidansa dake Abuja.

Sakon da Kwankwaso ya wallafa a shafinsa na Facebook ya bayyana cewa ya yi farin cikin karbar bakuncin a Aregbesola a gidansa dake Abuja.

A yan kwanakin nan dai ana cigaba da raɗe-raɗin cewa jagoran jam’iyar ta NNPP na duba yiyuwar shiga jam’iyar adawa ta APC tare da magoya bayansa.

More from this stream

Recomended