Sabon jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, ya bayyana cewa ƙasar za ta ɗauki fansar mutanenta da aka kashe a hare-haren da aka kai, ciki har da yara da ɗaliban makarantar Minab.
Khamenei ya bayyana hakan ne a cikin sanarwarsa ta farko tun bayan da aka naɗa shi a matsayin sabon jagoran addinin ƙasar. Gidan talabijin na gwamnatin Iran ne ya karanto sanarwar.
A cikin sanarwar, ya ce, “Dole ne mu nemi adalci ga mutanen Iran da suka rasa rayukansu a hare-haren da aka kai, za mu ɗauki fansa, ba za mu manta da jinin waɗanda aka kashe ba.”
Sabon jagoran ya kuma yi kira da a rufe sansanonin sojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.
Haka kuma ya jaddada cewa Iran za ta ci gaba da rufe mashigar ruwa ta Hormuz, yana mai cewa matakin na daga cikin hanyoyin da ƙasar za ta bi domin kare muradunta.
A ranar Litinin ne aka ayyana Mojtaba Khamenei a matsayin jagoran addinin Iran na uku. Hukumomi da cibiyoyi daban-daban na gwamnatin Iran, ciki har da gwamnati da ɓangaren shari’a da na tsaro da kuma sojoji, sun bayyana goyon bayansu tare da yi masa mubaya’a.
Wannan na zuwa ne a lokacin da rahotanni ke yawo a kafafen yaɗa labarai game da halin lafiyar sabon jagoran.
Sabon Jagoran Addinin Iran Ya Yi Barazanar Ɗaukar Fansa

