Ruwan sama mai ‘karfi da ya ɗau awanni yana sauka a ‘karshen makon da ya gabata ya yi sanadiyyar rushewar gidaje 184 a yankuna takwas da ke Karamar Hukumar Kurfi, Jihar Katsina.
Majiyar Sarauniya ta samu rahoton cewa bayan rushewar gidajen, ruwan ya kuma yi awon gaba da gonannakin mutane.
Yankuna takwas ɗin da ibtila’in ya auka wa su ne: Wurma, Birchi, Tsauri, Kofar Fada, Nasarawa, K’ofar Yamma, Sabuwar Unguwa da K’ofar Arewa.
Mutanen yankin sun ce an fara ruwan da misalin ‘karfe 1:15 na dare sannan ya tsaya da misalin ‘karfe 12 na rana. Hakan shi ya sa kogin da ke makwabtaka da su yayi ambaliyar da ta yi silar rushewar gidaje.
Wani ganau da ya nemi kada a ambaci sunanshi ya ce: “Gidaje 20 sun rushe a Wurma, 32 a Birchi, 23 a Tsari, 11 a K’ofar Fada, 19 a Sabuwar Unguwa, 32 a K’ofar yamma, 14 a K’ofar arewa, sannan kuma gidaje 43 a yankin Nasarawa.”