Rushe masallacin China ya jawo takaddama a Ningxia

[ad_1]

Masallacin Weizhou

Hakkin mallakar hoto
Weibo

Image caption

Masallacin na Weizhou wani kataferen gini ne mai kubbobi da hasumiyoyi, kuma an gina shi ne a salon gine-ginen gabas ta tsakiya

Daruruwan musulmi a yammacin China na takaddama da hukumomi domin hana rusa masallacinsu.

Jami’ai sun ce masallacin da a ka gama gininsa kwanan nan ba shi da takardun izinin gini a Ningxia.

Sai dai musulman sun ki amincewa, inda daya daga cikin mazauna garin ya ce ba za su “yarda gwamnati ta taba masallacin ba.”

China na da musulmi miliyan 23, kuma musulunci ya karbu a yankin Ningxia tsawon karni da dama da suka wuce.

Amma masu fafutikar kare hakki sun ce akwai karuwar nuna kiyayya ga Musulmi a China daga hukumomi.

An gina masallacin ne a wani salo na gabas ta tsakiya, inda ya ke da hasumiyoyi da kubbobi masu tsayi da dama.

Ya a ka fara boren?

Ranar 3 ga watan Agusta, jami’ai su ka buga wata sanarwa da ke cewa za a rushe masallacin da karfi da yaji saboda ba a bayar da izinin tsarawa da gina shi yadda ya kamata ba.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

‘Yan kabilar Hui na daya daga cikin manyan kabilu musulmai a China

An rarraba sanarwar a shafukan intanet tsakanin ‘yan kabilar Hui, kamar yadda kamfanin dillancin labarai ta Reuters ta ruwaito.

Mutane da yawa sun bukaci sanin dalilin da ya sa hukumomi ba su hana gina masallacin ba, wanda a ka gama shekaru biyu da su ka wuce, in dai har ba a bayar da takardun izinin gina shi ba, kamar yadda wata jaridar kasar Hong-Kong ta ruwaito.

Rahotanni sun nuna cewa an yi zanga-zanga a wajen masallacin ranar Alhamis kuma a ka ci gaba a ranar Juma’a. Hotunan da su ka bazu a shafukan sada zumuntan China sun nuna taron mutane mai dimbin yawa a wajen masallacin.

Har yanzu dai ba a tabbatar ba idan za a fara rushe masallacin ranar Juma’a kamar yadda a ka tsara, ko kuma idan an cimma matsaya.

Kafar watsa labaran kasar China ba ta ce komai ba har yanzu.

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...