Rundunar sojin saman Nigeriya ta musa zargin cewa ta jefa bam wa masu Maulidi a Kaduna

Rundunar sojin saman Najeriya ta musanta cewa tana da hannu a harin bam da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama a kauyen Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.

Wata majiya a Kaduna a wani rahoto da ta fitar ta yi zargin cewa jirgin da NAF ke aiki da shi ya bm da misalin karfe 9 na daren ranar Lahadi, lokacin da mutanen ƙauyen suka taru domin gudanar da bukukuwan Mauludi.

Lamarin ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Da take mayar da martani kan wannan ikirari, rundunar sojin saman ta bakin mai magana da yawunta, Air Commodore Edward Gabkwet, ya bayyana cewa NAF ba ta kai wani samame a Kaduna cikin awanni 24 da suka gabata ba.

Commodore Gabkwet ya ci gaba da tabbatar da cewa ba wai NAF kadai ce ke aiki da jiragen yaki marasa matuka a yankin ba.

More News

Dakarun Najeriya sun cafke wasu Æ´an’aiken Æ´anbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴanbanga sun sake kawar da wani ƙasurgumin ɗanbindiga

Rahotanni da ke fitowa daga Arewa maso Yammacin Najeriya na nuna cewa an yi nasarar kawar da wani fitaccen dan bindiga a jihar Zamfara,...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...