Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar cewa an kai wa sansanin sojojinta da ke harin garin Metele a jihar Borno hari.
Ta ce lamarin ya faru nea ranar 18 ga watan Nuwamba.
Ta kuma ce tana da kaidoji wajan fitar bayyanai kan sojojinta da suka rasa rayukansu kuma sai bayan ta sanar da iyalinsu ne take fitar da sanarwar akan duk wani abu ya faru da sojojinta.
Amma kuma ba ta bayyana adadin sojojin da aka kashe ba.
Sai dai ta ce ta lura da cewa akwai wasu kafofin watsa labarai da suka da na shafukan intanet da wasu jaridu da suka yi rahotannin da ta ce bai dai dai bane a kan yawan sojojin da suka rasa rayukansu tare da yadda hoton bidiyon da ta kira tsoho ne kan harin da aka kai wa sojojinta . Ta kuma bidiyon ba kuma bane illa farfaganda
Ta kuma ce karin sojojin da aka tura zuwa gari sun shawo kan lamarin kuma al’amura sun dai daita yanzu haka.
Sai dai bayan kusan mako guda ne da aukuwar lamari ne rundunar kasar ta fitar da sanarwar kuma wannna na zuwa ne bayan da Kungiyar ISWA wadda wani bangare na kungiyar BOKO Haram da ya balle ta wallafa wani bidiyo inda ta yi ikikari kai harin
Akwai rahotannin da cewa shugaba Muhammadu Buhari ya tura da ministan tsaron kasar Birgidiya janarar Mansur Dan Ali zuwa makobciya Chadi domin ya gana da shugaba Idris kan tababbarewar tsaro kan iyakar Najeriya da Chadin.