Rundunar Sojan Saman Najeriya Ta Kashe Abu Asad Jigo A Ƙungiyar Boko Haram

Bangaren sojan sama na rundunar Operation Hadin Kai ya sanar da kisan Abu Asad ɗaya daga cikin jagororin ƙungiyar Boko Haram.

Ƙarin ƴan ta’ada da dama aka bada rahoton sun mutu a harin da jiragen yaki suka kai musu a maboyar su dake Tagoshe a tsaunukan Mandara.

Edward Gabkwet daraktan yaɗa labarai na Rundunar Sojan Saman Najeriya shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa ranar Asabar a Abuja.

Gabkwet ya ce an kai farmakin ne a ranar Juma’a inda ya ce harin na daga cikin mafi nasara da bangaren sojan sama na rundunar Operation Hadin Kai ya kai a ƴan kwanakin nan.

Ya ce kafin kai harin sojojin saman sun ga ƴan ta’adda kusan sama da ɗari tare da wasu motocin yaƙi huɗu suna ta tattaunawa suna raha a tsakanin su a wurin dake da wasu gine-gine uku.

“Biyo bayan kai harin biyu daga cikin ginin sun rushe tare da dukkanin motocin yaƙin da aka lalata su”

“Akwai alamu dake nuna cewa Abu Asad wanda ƙusa ne a Boko Haram bangaren Ali Ngulde da kuma sauran yan ta’ada kamar su Ibrahim Nakeeb, Mujaheed Dimtu, Mustafa Munzir da sauransu na daga cikin ƴan ta’adda da dama da aka kashe a harin.” a cewar sanarwar.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...