[ad_1]
Rundunar ƴansandan Najeriya, ta bawa,Edwin Clark hakuri kan samamen da wasu ƴansanda suka kai gidansa dake Abuja.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya rawaito cewa Jimoh Moshood mai magana da yawun rundunar ƴansandan Najeriya shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da yafitar Abuja.
Moshood ya ce tuni aka tura wata tawagar ƴansanda zuwa gidan Clark ciki har da naibin babban sifetan ƴansanda mai kula da ayyuka da kuma wasu kwamishinonin ƴansanda.
Jaridar The Cable a ranar Talata ta rawaito cewa ƴansanda sun mamaye gidan Clark da misalin karfe 1:30 na rana bayan da suka nuna masa takardar izinin bincike.
Clark ya shedawa jaridar cewa babu wani abun laifi da suka samu a gidansa.
[ad_2]