Rundunar ƴan sandan jihar Niger ta tabbatar da mutuwar mutane 6 a harin ƴan bindiga

Rundunar ƴan sandan jihar Niger ta ce mutane shida aka kashe aka kuma yi garkuwa da wasu da dama biyo bayan harin da wasu yan bindiga su ka kai kauyen Tunga-Makeri da Konkoso dake karamar hukumar Borgu ta jihar.

Wasiu Abiodun mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya fadawa jaridar The Cable cewa sun samu labarin kai harin da karfe 06:00 na safiyar ranar Juma’a.

A cewarsa maharan sun biyo ta gundumar Shafaci inda su ka farma kauyen Tunga-Makeri da misalin karfe 03:00 na dare.

“Mutane 6 ne suka rasa rayukansu an kuma kona wasu gidaje tare yin garkuwa da wasu mutane da kawo yanzu ba a san yawansu ba.

Abiodun ya tabbatar da cewa daga baya yan bindigar sun je kauyen Konsoko amma basu da cikkaken bayanai kan harin.

Sai dai wasu mazauna ƙauyukan sun bayyana cewa yawan mutanen da aka kashe ya haura 32.

More from this stream

Recomended