Rikici ya ɓarke a Abuja inda ƴan jari bola suka kashe mutane 3

Rahotanni sun ce an kashe mutane uku da suka hada da mata biyu da yaro daya a wata arangama da aka yi tsakanin ‘yan iskan gari da ake kira baban bola da mazauna unguwar Byazhin a Kubwa a karamar hukumar Bwari ta babban birnin tarayya Abuja.

Wata shaidar gani da ido, wacce ta bayyana kanta da Jessica Adam, ta shaida cewa, wani baban bola ya yi yunkurin satar tukunyar miya ta wata mata, amma abin ya ci karfinsa kuma an lakada masa duka bayan matar ta sanar da makwabta da masu wucewa.

Baban bolan wanda ya harzuka ya tafi ya tara ‘yan iskan da suka dawo da misalin karfe 8 na dare dauke da makamai da suka hada da adduna, kulake, da duwatsu, suka fara kai wa mazauna garin hari ba kakkautawa, inda suka kashe matar da aka sace wa tukunyar miyar.

A harin, an kashe wasu mutane biyu, mace da wani yaro matashi, wadanda aka ruwaito cewa masu wucewa ne.

A halin da ake ciki, kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ya ci tura, domin an kasa samun lambarta.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...