Rikici ya ɓarke a Abuja inda ƴan jari bola suka kashe mutane 3

Rahotanni sun ce an kashe mutane uku da suka hada da mata biyu da yaro daya a wata arangama da aka yi tsakanin ‘yan iskan gari da ake kira baban bola da mazauna unguwar Byazhin a Kubwa a karamar hukumar Bwari ta babban birnin tarayya Abuja.

Wata shaidar gani da ido, wacce ta bayyana kanta da Jessica Adam, ta shaida cewa, wani baban bola ya yi yunkurin satar tukunyar miya ta wata mata, amma abin ya ci karfinsa kuma an lakada masa duka bayan matar ta sanar da makwabta da masu wucewa.

Baban bolan wanda ya harzuka ya tafi ya tara ‘yan iskan da suka dawo da misalin karfe 8 na dare dauke da makamai da suka hada da adduna, kulake, da duwatsu, suka fara kai wa mazauna garin hari ba kakkautawa, inda suka kashe matar da aka sace wa tukunyar miyar.

A harin, an kashe wasu mutane biyu, mace da wani yaro matashi, wadanda aka ruwaito cewa masu wucewa ne.

A halin da ake ciki, kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ya ci tura, domin an kasa samun lambarta.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...