Rashin Kudi Ya Kashe Kasuwar Raguna A Adamawa

[ad_1]

Duk da cewa bana-farashin raguna sun sauka sosai idan aka kwatanta su da bara, masu sayar da raguna na fama da rashin kasuwa wanda suka danganta da rashin kudade a hannun jama’a.

Ahmadu Aliyu, wani mai sana’ar dabbobi ne a Jalingo fadar jihar Taraba, ya bayyana cewa akwai saukin dabbobi a bana, lamarin ya fi na bara idan har aka kwantanta da yadda kasuwar ke gudana, inda yace ma akwai raguna masu sauki da mutum zai iya saye gwargwadon wadatarsa.

Shi ma wani dillalin dabbobi ya danganta tsadar a yanzu da yan baranda da kuma tashe tashen hankulan da aka yi fama da shi da cewa su suka jawo tashin gwauron zabin.

To sai dai kuma, Mallam Muhammad Tukur Misa, wani magidanci ne da ya zo sayan ragon layya,yace duk da halin da ake ciki, shi kan tabarkallah.

Malam Ahmadu Gassol wani magidanci mai ya’ya biyu dake shirin hidimar sallah, ya bayyana cewa lallai akwai tsananin rashin wadatan kudade a hannayen jama’a, ga rashin biyan albashi, to amma duk da haka za su kokarta, domin samun lada.

A halin yanzu dai ma’aikata ma na kuka da rashin biyansu albashi ta yadda suke gwagwarmayan ganin sun yi hidimar sallah ko da kuwa da bashi ne in sun samu albashin su biya. Yayin da a bangare guda, ake iya ganin cincirindon jama’a a bankuna suna kokarin cire kudaden ajiyansu domin gudanar da shiye-shiryen sallah.

A saurari rahoton Ibrahim Abdulaziz

[ad_2]

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...